16/03/2025
ALAMOMI NA NUNA CEWA AN KADA GANGAR SIYISAR NAJERIYA TA 2027!
A kwanakin nan ne dan shugaban kasar Najeriya Seyi Tinibu ya fara wata rangadi zuwa jahohin kasar, inda aga gansa yana ziyartar masarautu, malumma 'yan siyasa da kuma shirya taron shan ruwa a kewaye da 'ya'yan gomnoni da masu ruwa da tsaki a gomnatocin ta tarayya dana jihohi da kuma shugannin matasa da kuma mawaka don rakiya, qarfafawa da nuna gogon ga abunda yazo ashi, ana masu wakoki da bambadanci shi da ubanshi, ya kuma raba masu abinchi!
A wani bangaren kuma ana ta rade-radin wasu jigajigan siyasar jihohi da masu ruwa da tsaki a jam'iya mai mulki da na adawa kamar tsoffin gomnoni, ministoci da komishinoni da ma suna ta shirye shiryen tsallen sauya sheka daga jam'iyoyinsu zuwa wasu. Wasu don komawa mai mulki wasu kuma don barin mai mulki. Kowa da korafinsa na rashin samun biyan bukatunsa a gomnatance, jam'iyance ko a Najeriyance ga wadanda suke ikrarin suna siyasar don cigaban kasa da walwalar don kasa kenan!
Abunda yafi yamutsa hazo a kwanakin nan a kafafren sada zumunta shine fircewar fitaccen dan gwagwarmayar siyasa a Najeriya, daya daga cikin 'yan gaba a kafa APC, kuma tsohon gomnar jihar Kaduna wato mallam Nasir El-Rufai daga jama'iyar APCn zuwa SDP.
Wanda tun kafin ficewar tasa yata nuna rashin gamsuwarsa ga yadda APCn take tafi da lamarin jagorancin gomnatin kasar, jihohi da kuma lamarin jam'iyar. Inda yace gaba daya sun sauka daga kan tsarin gudanarwa ta jam'iya wanda shine; tsaro, lafiya ilimi, dakile rashawa, lantarki walwala da sauransu. Wadannan suna daga cikin lamurran da s**a kara saka ruwa tsami tsaninsa da aminansa na gomnatocin tarayya dana jiha, kamar gomnar jihar Kaduna wanda El-Rufain ne yayi uwa yayi makarbiya wajen daurashi a karagar jagorncin jihar bayan kammala wa'adinsa, wanda a kwanakin kuma aka jiyo El-Rufain yana masa Allah Ya isa da tsinuwa bisa amfani da jamian tsaro da gomnar keyi don gallaza masa shi da mutanensa gami da tsare wasu akeyi babu dali a cewarsa.
A yayinda a wasu gurare aka jiyo yana kiran amininsa kuma surukinsa, mai baiwa shugaba Tinubu shawara kan harkar tsaro, Nuhu Ribado, ba mutum bane, mara amana, makaryachi da dai sauransu.
An kuma kara jiyo shi yana kira ga jigogin adawar siyasar Najeriya kamar su: Alh. Atiku Abubakar, Peter Obi, Rotimi Amechi da sauransu da su shiga SDP don su hada karfi da karfe don fatattakar gonmatin APCn! Ko hakan mai yiwuwa ne?