20/12/2025
Wata macijiya tana kukan neman agaji bayan wani dutse ya fāɗo mata.
Sai wata mata ta zo daga nesa ta taimake ta ta cire dutsen daga kanta.
Bayan ta taimake ta, sai macijiyar ta ce:
"Na rantse zan sari duk wanda ya taimake ni."
Sai matar ta ce:
"Ni na taimake ki, amma kina shirin cutar da ni?"
Macijiyar ta ce:
"Zan sare ki kuma ba zan ji tausayinki ba. Wannan halina ne, kuma hali na baya canzawa."
Matar ta ce:
"To, bari mu tambayi dabbar farko da muka hadu da ita a hanya. Idan ta ce kina da gaskiya, to ki sare ni."
S**a ci gaba da tafiya har s**a hadu da zakin nan na daji, wolf, (kyarkeci)S**a ba shi labarin daga farko zuwa ƙarshe.
ya ce:
Ba zan yarda da ku ba har sai kun sake nuna min abin da ya faru da ido na."
Sai matar ta ɗauki dutsen ta sa a kan macijiyar, ta ce:
"Haka na same ta."
Sai kyarkecin ya ce:
"To, bar ta a haka kamar yadda kika same ta. Wanda baya godiya bai cancanci a taimake shi ba. Wanda ya saba da rashin nuna godiya ba zai taɓa canzawa ba komai yadda ka yi masa alheri."
Darasi:
Ba kowa ne da za ka yi masa alheri zai yaba ba. Kuma wanda ya saba da jin kai da rashin godiya, ko ka sadaukar da kanka, ba zai canza ba.
Kamal Bin Mansur ✍️