15/05/2026
Muna sanar da jama’a cewa mu, Lauyoyi Masu Kare Hakkin Jama’a, mun shigar da kara gaban Babbar Kotun Jihar Zamfara da ke Gusau don kalubalantar cin zarafi da take hakkin bil’adama da jami’an hukumar ZAROTA ke yi wa mutane.
Wannan mataki ya biyo bayan wani lamari da ya faru ranar 28 ga Fabrairu, 2026, a Sabon Gari, Gusau, inda jami’an hukumar s**a ci zarafin lauya sannan s**a kwace masa waya saboda kawai yana daukar hoton yadda suke take hakkin jama’a a fili.
Abubuwan da muke bukata a gaban Kotu:
Hakin Daukar Hoto: Kotu ta tabbatar da cewa dan kasa yana da ikon daukar hoton ma’aikacin gwamnati yayin da yake gudanar da aiki a fili.
Hana Kwace Kaya: Kotu ta bayyana cewa ZAROTA ba ta da ikon kwace kadarorin mutane (kamar waya) ba tare da umarnin kotu ba.
Daina Cin Zarafi: A dakatar da duka, tsoratarwa, da gudanar da aiki ba tare da katin shaida ko kakin sani ba.
Neman Hakki: Muna neman kotu ta tilasta wa ZAROTA ba da hakuri a fili, sannan ta biya diyya kan keta haddin da ta yi.
"Hakkin dan adam ba ihisani ba ne; rantsattsen tanadi ne na kundin tsarin mulki wanda kowace hukuma dole ne ta girmama shi."
Wannan karar mataki ne na tabbatar da cewa babu wata hukuma a Jihar Zamfara da ta isa ta kasance sama da doka.
Sa hannu:
M. Umar, Esq. & M. Sani Kaura, Esq.
(Lauyoyi Masu Kare Hakkin Jama’a)
14.05.2026
======================
We filed LAW Suit Against the ZAROTA
We the Public Interest Lawyers have formally filed a Fundamental Rights Enforcement Suit at the High Court of Zamfara State (Gusau Judicial Division) against ZAROTA
This legal action targets the systemic abuse of power and persistent unlawful conduct by officers of the **Zamfara State Road Traffic Agency (ZAROTA)*.
The suit originated from an incident of **February 28, 2026, at Sabon Gari, Gusau* wherein ZAROTA officers harassed me and forcibly seized my mobile phone for documenting their act of Human rights violation activities in a public space.
The case would serve as a judicial challenge to a broader pattern of human rights violations of ZAROTA's marshals during road operations especially in Gusau the state capital.
We equally invite the court to affirm and declare the following:
1- Constitutional Right to Record:That citizens have a protected right to document public officers performing their duties in public spaces.
2- Prohibition of Illegal Seizures:That ZAROTA lacks the statutory authority power to seize private property, including mobile phones, without a valid court order.
*3- Cessation of Abuse:* That acts of assault, threats, and intimidation constitute direct violations of the 1999 Constitution (as amended).
4- Mandatory Identification: That operating without visible uniforms or identification tags violates the *Zamfara State Road Traffic Agency Law, 2015, and undermines public accountability.
*We further also demand the following Reliefs: to include Perpetual Injunction:* A court order permanently restraining ZAROTA from future harassment or unlawful seizure of citizenaproperty.and seek for Public Apology formal from the Agency. While urging the court also for Exemplary Damages by way of Financial compensation for the gross violation of the Applicant’s fundamental Rights.
"Fundamental Rights are not privileges granted by the state; they are constitutional guarantees that every authority is bound to respect."
This suit is a commitment to ensuring that no agency in Zamfara State operates above the law. We remain dedicated to reinforcing transparency and the Rule of Law for a better Zamfara and beyond.
Signed:
M. Umar, Esq.
M. Sani Kaura, Esq.
*(Public Interest Lawyers & Human Rights Advocates)*
[email protected]
14.05.2025